Ƙungiyar masu dakon man fetur a Naijeriya ta NATO ta ce akwai yiwuwar ƙarancin man fetur da ake fuskanta a wasu sassan ƙasar ya ta’azzara idan ba a kammala gyaran hanyoyi da ake yi ba.
Bayan taron da manyan kamfanoni da sauran masu faɗa-a-ji kan harkokin man fetur suka gudanar a birnin Legas ranar Laraba, ƙungiyar ta ce idan ana bukatar kawo karshen matsalolin man fetur baki ɗaya dole ne gwamnatin tarayya ta farfaɗo da matatu da bututan da ke aikewa da fetur zuwa jihohi.
Wakilinmu na Legas Umar Shehu Elleman ya tattauna da Alhaji Yusuf Lawal Usman, shugaban kungiyar ta masu dakon mai.