Addu’a ce za ta Kawo karshen tashe-tashen hankula a kasar nan: Janar Babangida

Tsohon shugaban kasa na mulkin soji Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya ja hankalin  al’ummar kasar nan da su ci gaba da hada kai domin Najeriya ta ci gaba da kasancewar a matsayin kasa guda.

Babangida ya yi jan hankalin ne a zantawa sa da manema labarai a lokacin murnar cikarsa shekaru 81 a duniya ya ce hakuri shine babban abinda ya kamata ‘yan Najeriya  su rike domin cin moriyar juna duk da banbancin yare da addini dake a tsakanin al’ummar Najeriya.

A fannin tsaro da ya addabi sassan kasar nan  kuwa babangida ya ce a ci gaba da addu’a kuma akwai lokacin da lamarin zai zama tarihi ga kasar nan.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments