Muna taya mai martaba murnar maimaituwar wannan rana Abubakar kofar na’isa

Mai martaba sarkin kano na 15 a jerin sarakunan fulani Alhaji aminu ado bayero ya samu kansa a wannan duniya a ranar 21-8-1961 inda a daidai wannan rana yake cika shekara 61

Daga wakilin aksammedia B.imam

Mai martaba sarkin kano kamin ya hau kan kujerar mulkin gidan dabo ya rike mukamai na sarauta daban daban kamar yadda aka sani duk dan sarki indai ya cancanci a nada shi sarauta ana nada shi mai martaba saida ya rike mukamin wanban kano sannan Allah ya daga likkafar sa zuwa sarkin bichi na farko a tarihi bayan ya idda shekarun da Allah yasa zaiyi a bichi ne sai mai girma gwamnan jihar kano ya nada shi a matsayin sarkin kano na 15 a jerin sarakunan fulani

Mai magana da yawun masarautar kano abubakar balarabe kofar na’isa ya shiga sahun masu taya mai martaba murnar cika wadannan shekaru

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments