Buhari na shirin gana da hafsoshin tsaro kasar nan a yau Litinin

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai yi taron gaggawa da manyan jami’an tsaro a Abuja a ranar Litinin.

Wata sanarwa da kakakinsa, Malam Garba Shehu ya fitar a karshen mako, ta ce taron zai mayar da hankali ne kan yadda za a karfafa matakan tsaro a sassan kasar.

Taron zai wakana ne bayan da Amurka ta fitar da wata sanarwa da ke cewa akwai yiwuwar akai hare-hare a wasu sassan kasar, ciki har da babban birnin tarayya Abuja.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments