Zamuyi du mai yuwuwa wajan ganin Atiku da jam’iyar PDP sun yi nasara a kowacce kujera: cewar kungiyar “Atiku Solution”

An bayyana Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar a matsayin mutumin da zai iya kawowa kasar nan cigaban da ya dace cikin kankanin lokaci.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar “Atiku Solution”  ta kasa reshen jihar Kano, Eng Umar Mai Dabino  ya fitar bayan kammala taron da kungiyar da gudanar a yau Lahadi 23-10-2022.

Mai Dabino yace kamata yayi mutane su dawo daga rakiyar jam’iyar mayaudara da suka jefa  yan Najeriya a cikin mawuyacin hali na kunci da takura.

Taron ya Sami halartar shugabannin kungiyar daga sassan jihar Kano kuma ya gudana ne da yawun shugaban ta na kasa ENG.  JANKARA

 

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments