Za mu janye yajin aiki nan ba da jimawa ba – ASUU

Daga Walid Hari

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya, ASUU, Farfesa Victor Emmanuel Osodekeya ce nan ba da jimawa za su koma azuzuwa domin ci gaba da koyarwa.

Ya bayyana haka ne yayin da ya gana da kakakin majalisar wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila ranar Litinin.

Farfesa Osodeke ya yaba wa matakin da majalisar wakilan kasar ta dauka na shiga tsoma baki domin ganin an yi sulhu tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU wadda ta kwashe wata takwas tana yajin aiki.

Wani bidiyo da aka wallafa a shafin Tuwita na majalisar wakilan Najeriya ya nuna Farfesa Osodeke yana cewa sun kusa kawo karshen yajin aikin.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments