Yunkurin juyin mulki a kasar Chadi ya bar baya da ‘kura

Gwamnatin kasar Chadi ta ba da sanarwa a jiya Alhamis cewa, jami’an tsaron kasar, sun yi nasarar murkushe wata makarkashiya da wasu sojojin kasar suka kitsa  ta hambarar da gwamnati mai ci.

Sanarwar ta ce, jami’an soja 11 ne, suka kitsa wannan makarkashiya da ta zama barazana ga tsaron kasar.

Gwamnatin Chadi ta ce, an kama wadanda suka aikata laifi, ana kuma gudanar da bincike a kan su.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments