Yanzu-yanzu ICPC ta kama wani matashi da Naira miliyan biyu na siyen kuri’u
Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa da sauran ayyuka masu alaka da cin hanci ta ICPC ta tabbatar da kama wani matashi dauke da Naira miliyan biyu da yake niyya kaiwa wani Dan siyasa a jihar Gombe.
Jami’ar hulda da jama’a ta Hukumar Azuka Ogugua ta tabbatar da faruwar lamarin inda tace kudin sun hadar da tsoffi da sabbin takardu
Tace jami’an hukumar ta su masu kewayen ko ta kwana akan manyan tituna sune suka kama matashin mai suna Ahmad a Alkaleri dauke da tsoffin takardun kudi na 900,000 sai kuma sabbin takardun kudi na 1.1 miliyan kuma tuni suka damka shi a hannun jami’an hukumar ta su da Bauchi