Yan bindiga sun sake aika sako mai daga hankali ga iyalai da yan uwan kwamishinar hukumar kidaya ta kasa

Yan bindigan sun yi awon gaba da kwamishinar yayin da take kan hanyar zuwa Patakwal, babban birnin jihar Ribas daga garin Brass na jihar Bayelsa

Rahotanni sun nuna cewa maharan sun sace kwamishinar ne tare da Direbanta da kuma yar aikinta a kan hanyar zuwa garin Fatakwal

jaridar punch ta ruwaito cewa maharan sun sace matar, direba da mai aikinta da misalin ƙarfe 6:30 na yamma ranar Lahadi bayan ta dawo daga ƙarar hukumar Brass.

A halin yanzun wasu bayanai sun nuna cewa masu garkuwa da Misis Izonfuo sun aiko da saƙo, sun nemi miliyan N500m a matsayin kuɗin fansa.

Jami’ar hulÉ—a da jama’a na rundunar ‘yan sanda reshen jihar Ribas, Grace Iringe-Koko, ya tabbatar da sace kwamishinar NPC ta Æ™asa.

Ya Æ™ara da cewa kwamishinan hukumar ‘yan sandan jihar ya tashi tawaga ta musamman kuma ya É—ora musu alhakin tabbatar da cewa wacce aka sace ta kubuta lami lafiya

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments