An yaba da kokarin hukumar hisbah ta jihar kaduna bisa dagewar ta wajen habaka ayyukan kirki da dakile barna kamar yadda dokokin hukumar hisbah ta jihar ya tanada.
Yabon ya fito ne ta bakin kwamanda hisbah na jihar Kano, Sheik Haroon Muhammad Sani a garin Kaduna.
Ibn Sina ta bakin mataimakinsa a bangaren horas da dakarun hisbah malam Idris ibn Umar Wanda ya wakilci kwamandan hisbah.malam Idris ibn Umar yace Babbar nasara CE daukan dakarun hisbah a karamar hukumar zari”a ta jihar kaduna wanda zai taimakawa gwamnatin jihar a fuskar dakile badala.
Malam ibn Umar ya ce adadin sababbin dakarun su Saba,in da biyar a yankin karamar hukumar ta zazzau malam idris ibn Umar yace sakon sheik ibn sina shine kofarsa sa a bude take domin neman shawara ko wani taimako akan cigaban aiyukan hukumar hisbah a kowane sashe na kasar Nan.