Yadda sojoji suka yi artabu da wasa jagororin masu garkuwa da mutane a Kaduna

Yadda sojoji suka kashe wani jagoran masu garkuwa da mutane a Kaduna

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe wani jagoran yan taadda mai suna Isyaku Danwasa.

Rundunar ta bayyana hakan ne a shafin ta na Twitter wanda laftanal kanal Musa Yahya ya wallafa

Sanarwar tace jami’an sojin sun Sami bayanan sirri akan yan ta’addan kafin faruwar lamarin kuma suka rutsa su a gurin da suke sayen alburusai inda suka harbe su a take a gurin.

Rundunar ta ce an Sami Bindugu kirar Ak 47 da alburusai masu yawa da kuma kudi Naira 200,000 sai mashin guda daya da aka kone shi

A nasa bangaren shugaban dake kula da ayyukan rundunar. Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya yaba da kokarin jami’an kuma yace ba zasu ragawa duk wani Dan taadda ba

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments