Yadda masana suka yi fashin baki akan jawabin shugaba Buhari na barin gado

Daga khadija Salisu Danmaliki

Jawabin bankwana da shugaban Najeriya mai barin gado, Muhammadu Buhari, ya gabatar a safiyar Lahadi cike yake da alfahari da kuma neman afuwar ‘yan Ć™asa game da rayuwar shekara takwas a Ć™aragar mulkinsa.

ĆŠaya daga cikin É“angarorin da shugaban ya ce yana alfahari da shi shi ne zaÉ“ukan da Ć™asar ta gudanar a Ć™arĆ™ashin mulkinsa – na 2019 da kuma na watan Fabarairu.

“A matsayinmu na Ć™asa, wajibi ne mu É—ora a kan nasarorin da muka samu a harkokin zaÉ“e don Najeriya ta samu matsayin da ya dace a tsakanin Ć™asashen duniya,” in ji shi.

“Don tabbatar da cewa dimokuraÉ—iyyarmu ta ci gaba da inganta kuma ‘yan siyasarmu sun zama adalai, na gina tsarin zaÉ“en da Ć™uri’u ke yin tasiri, sakamakonsa ke da inganci, mai cike da adalci wanda kuma ba a fiya amfani da kuÉ—i ba. Kuma ‘yan Najeriya za su iya zaÉ“ar shugabannin da suke so.”

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments