Talakawa na ci gaba da zanga-zangar adawa da karin kudin haraji a kasar Kenya

Ƙasar kenya ta jajirce wajen gudanar da zanga-zangar adawa kan tsadar rayuwa da ƙarin haraji, lamarin da ya rikiɗe zuwa tashin hankali, inda aka kashe akalla mutum 24 a ƴan watannin nan.

A lokacin zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a bara, James Wainaina, direban tasi a Nairabo babban birnin ƙasar, ya zaɓi William Ruto, wanda ya bayyana kansa a matsayin ɗan takarar abin da ya kira ‘ƙasar da take fafutika da harkar tattalin arziki’.

Amma yanzu Mista Wainaina yana jin an ci amanarsa kuma yana goyon bayan zanga-zangar.

BBC hausa ta ruwaito cewa tun lokacin da shugaba Ruto ya hau karagar mulki, farashin kayayyaki ke ci gaba da hauhawa yayin da kuma gwamnatinsa ta ƙara haraji.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments