Sojoji 15 da Yan sanda biyar sun rasa rayukan su a wani Hari da Yan bindiga suka Kai musu

Wasu da ake zargin Yan bindigar ne sun bindige jamian tsaro kimani su 20 da suka hada da sojoji 15 da Yan sanda biyar a jihar Kebbi.

Lamarin ya faru ne a karamar hukumar Zuru ta jihar Kebbi kana ya hada da garuruwan Kanya da Danko-Wasaga.

Rahoton ya bayyana cewa sojojin da suka rasa rayukan su sun fito ne daga bataliyar Light Tank ta sojin Najeriya.
A makon da ya gabata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi Allah wadai da irin wadannan ayyukan Yan taadda a jihar ta Kebbi biyon bayanan kashe mayakan sa kai  68 da Yan taaddan suka Yi a jihar ta Kebbi.
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments