Rundunar soji da Al’ummar kasar Niger sun goyi bayan juyin mulkin da aka yiwa Bazoum

Magoya bayan juyin mulkin sojoji a Nijar sun kai hari kan shalkwatar hamɓararren shugaban ƙasar, inda suka cinna wuta tare da jifa da ƙona motocin da ke gaban ginin.

Rukunin masu cinna wutar sun ɓalle ne daga cikin wasu ɗumbin mutanen da suka yi dandazo a gaban ginin majalisar dokokin ƙasar don nuna goyon baya ga sojoji masu juyin mulki, inda aka ga wasu na ɗaga tutocin Rasha.

Rundunar sojojin ƙasar a yanzu ta mara baya ga dakarun da suka ƙwace mulki kuma suke tsare da Shugaba Mohamed Bazoum tun ranar Laraba.

Rasha ta bi sahun sauran ƙasashen duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya wajen kira a saki Bazoum.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments