Home HAUSA NEWS Rikici na shirin kunno kai tsakanin Amurka da kasar China kan batun...

Rikici na shirin kunno kai tsakanin Amurka da kasar China kan batun Taiwan

Ministan tsaro na kasar China Janar Wei Fenghe, a jawabin sa na taron kolin  kasa da kasa karo na 19,  Dan tattaunawa kan harkokin tsaro da tsaro na Asiya karo na 19 a Singapore, ya jaddada aniyar kasar sa na cigaba da tsara kasar Taiwan tare da hana ta yancin kai.

 

Kasar China tace za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin ta hana Taiwan samun ‘yancin gashin kanta, matakin da ke kara rurura wutar rikici tsakaninta da Amurka kan yancin tsibirin.

Ministan  tsaron kasar China ya sha alwashin me a jiya Lahadi, yana mai cewa kasar baza ta amince ba har sai inda karfinta ya kare.

Amurka da China na musayar kalamai kan tsibirin mai cin gashin kansa, wanda Beijing ke kallonsa a matsayin wani yankinta dake jiran sake hadewa.

Kutsawar jiragen saman kasar China kusa da yankin Taiwan ya kara dagula yanayin diflomasiyya tsakanin kasashen biyu masu karfin fada aji.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments