MDD ta magantu gameda dubban yan gudun hijira daga Sudan

Dubun dubatar ‘yan Sudan sun yi gudun hijira don tserewa yaki da rashin tsaron da ƙasar ke fuskanta cikin kwanakin nan.

MDD da sauran kungiyoyin agaji sun yi kiran a kawo musu ɗaukin gaggawa a halin da suke ciki.

Jaridar BBC ta ce yawancin mutanen na guduwa ne zuwa wasu ƙasashe makwaɓta kamar Sudan ta Kudu da Habasha da Chadi da Masar da kuma Djibouti.

A jiya Laraba, shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya Dr Tedrus Adhanum Gebreyesus da ke halartar taro a Geneva, ya bayyana mummunan halin da Sudan ke ciki, inda ya ce hakan zai sake janyo taɓarɓarewar fannin lafiyar ƙasar da ya kusan durkushewa.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments