Kasarsa kalamai na karuwa tsakanin China da Amurka

Mai magana da yawun ma’aikatar tsaron kasar China, Tan Kefei, ya amsa tambayoyin ‘yan jarida game “balan balanced ta leken asiri” ta kasar.

Kefei a wani taron manema labaru da aka shirya a yau Alhamis yace Yana mai adawa da kalaman rashin gaskiya da wasu mutane ke furtawa a Amurka, tare da fatali da gaskiyar lamari.

Ya ce, tarihi ya tabbatar da cewa zai ci gaba da tabbatar da cewa, a ko da yaushe sojojin kasar Sin sun kasance masu tsayin daka wajen aiwatar da ayyukan tabbatar da tsaro a duniya, da yin hidimar gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bli-Adama.

Ya kara da cewa, kasar Sin a ko da yaushe tana tsayawa kan manufar kasancewa wadda ba za ta taba fara amfani da makaman nukiliya a kowane lokaci, a kowane hali, kuma ta yi alkawarin ba za ta yi amfani da makaman nukiliya ba, ko kuma ta yi barazanar yin amfani da makaman nukiliya a kan kasashen da ba su da makamin nukiliya, da kuma yin barazanar yin amfani da makaman nukiliya kan yankunan da ba su da makamin nukiliya

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments