Hukumar Tsaron ta jar-kwala ta kame yan Daba 55 a Kano

Hukumar dake sa Ido kan kadarorin gwamnati ta tabbatar da kama wasu da ake zargi yan bangar siyasa ne su 55 a yankin karamar hukumar kumbotso dake jihar Kano

Hukumar ta tabbatar da hakan ne ta bakin jami’in hulda da jama’a na Hukumar Ibrahim Abdullah

Abdullahi yace jamian su sun kai samame ne a dai-dai lokacin da suka sami labarin yan Daba su farmaki al’ummar yankin Na’ibawa tare da kone motocin mutane

Kazalika yace sun kwace muggan makami a hannun yan Dabar da suka kama

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments