Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar China, Mao Ning, ta gabatar da jerin gudummawar da kasar China ta bayar domin bunkasar tattalin arzikin duniya a cikin shekaru 10 da suka gabata,
Ning ta bayyana hakan ne a lokacin wani taron manema labarai da aka saba gudanarwa a Lahadin da tagabata.
Ta bayyana cewa, kasar Sin za ta kara ba da gudummawa wajen samun ci gaban tattalin arzikin duniya mai karfi, da dorewar daidaito da wanda zai shafi duniya baki daya.