Jam’iyar APC ta shiga taron gaggawa bayan murabus din tsohon shugaban jam’iyyar

Mambobin kwamitin gudanarwa (NWC)na jam’iyyar APC ta ƙasa zasu sa labule da gwamnonin jam’iyyar yau Laraba, 19 ga watan Yuli, 2023 a birnin Abuja.

NWC zata gana da gwamnonin ne a wani yunƙuri na neman goyom baya daga manyan masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC bayan murabus ɗin Abdullahi Adamu.

Wannan taro na zuwa ne awanni 48 kacal bayan mataimakin shugaban APC na shiyyar arewa, Abubakar Kyari, ya karbi ragamar jam’iyya a matsayin muƙaddashin shugababa.

Hakan ta faru ne bayan shugaban APC na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, da sakatare na ƙasa, Iyiola Omisore sun yi murabus daga kan muƙamansu.

A wurin taron da NWC ya gudanar ranar Litinin, an cimma matsayar zaama da masu ruwa da tsaki kan abubuwan da ke faruwa a cikin gida

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments