Jam’iyar APC ta magantu akan tsanantar rashin lafiyar gwamnan ta, Rotimi Akeredolu

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu ya yi magana a karon farko game da halin da Gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu yake ciki.

Jaridar This Day ta ruwaito Sanata Abdullahi Adamu yana cewa Mai girma Rotimi Akeredolu yana kwance a asibiti, har ta kai ba zai iya tabuka komai a yanzu ba.

Shugaban APC mai-mulkin kasa ya yi  wannan bayani ne a zaman da yayi da ‘yan Majalisar NWC da shugabannin jam’iyya na jihohi.

Jam’iyyar APC ta tabbatar da halin rashin lafiyar da Gwamna Rotimi Akeredolu yake fama da ita, yana jinya a asibitin kasar waje.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments