INEC ta soke sakamakon wasu rumfunan zabe a jihar Kogi

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta wallafa cewa tayi watsi da sakamakon wasu rumfunan zabe da aka samu hatsaniya yayin gudanar da zabe a guraren a jihar Kogi.

Kwamishinan hukumar dake tattara sakamakon zaben jihar Kogin Dacta Hale Longport, shine ya sanar da hakan inda yace lamarin soke zaben zai hada da wasu kananan hukumomi

A zantawar sa da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN yace sun Sami rahoton ayyukan Daba yayin gudanar da zaben wasu gurare da suka hada da Anyigba da Dekina a karamar Hukumar Kogi ta Gabas da mazabar Mopa a Kogi ta yamma da kuma wasu bangarorin karamar hukumar Kogi ta tsakiya.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments