Hukumar kula da kadarorin gwamnati ta kama miliyoyin kudin Bogi a wasu jihohi

Hukumar tsaro ta jar kwala taci alwashin yaki da masu yin kudin Bogi

Hukumar dake kula tare bada tsaro ga kadarorin gwamnati ta jar-kwala taci alwashin kama tare da gurfanar da duk wanda ta samu yana ta’ammali da kudin jabu a gaban kotu.

Shugaban Hukumar na kasa Ahmed Audi shine ya bayyana hakan a zantawar sa da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN

Yace hukumar sa ta jar-kwala ba zata yi kasa a guiwa ba wajen sintirin tare da kama duk wanda ta samu da taadar yin zagon kasa ga tattalin arzikin Najeriya

Ya kara da cewa kawo yanzu hukumar sa ta kama miliyoyin kudaden jabu a jihohi da dama na kasar nan.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments