Har Yan zu Al’umma Na Cigaba Da Tururuwa Zuwa Gidan: Marigayi Alhaji Uba Leader

Al’ummar kasan nan su yi matukar kadowa sakamakon rashe babban dankasuwa, dan siyasa kuma Malamin Addinin Musuluchi Alhaji Uba Leader. A ranar Asabar 21 ga watan August, 2022 Allah Ya yi wa marigayin rasuwa bayan ya yi fama da gajeriyar rashe lafiya a Asibitin Zenith Clinic da barin Kano.

Kafin rasuwarsa shi ne shugaban Kamfane Masaka Texts stall dake unguwar Gwammaja a jihar Kano

Shi ma Shugaban Kasar Muhammadu Buhari ya mika sakon ta’aziyarsa ga ‘iyale da ‘yan uwa da saurar al’ummar kasannan musamman ma Na jihar Kano, a wata sanarwa da mai magana da yawunsa Malam Garba Shehu ya rabawa manema labarai, a Abuja yace shugaban ya yi matukar kaduwa bisa wannan babban rashi.

Alhaji Uba Leader, ya rasu ya bar ‘yan 34 maza da mata da kuma jikoki da dama, tuni a ka yi jana’izarsa kamar yadda Addinin Musuluchi ya tanada

 

 

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments