Hadarin babbar Mota yayi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 20 a jihar Kogi

Wata mota da ta dauko man fetur tayi hadari a gadar Ankpa inda aka samu wani mummunan hadari ya yi sanadiyyar dinbin mutane sun mutu

Lamarin ya faru ne a wata gada da ke garin Ankpa, jami’an FRSC sun tabbatar da afkuwar lamarin

Fiye da mutum 20 ake tunani sun rasa rayukan su sanadiyar kifewa da wata babbar mota tayi a kan wata gada a jihar Kogi.

Jaridar  Daily Trust tace a safiyar Alhamis, 29 ga watan Satumba 2022. babbar mota ta fadi a wata gada da ke kan ruwan Maboro a karamar hukumar Ankpa a jihar Kogi.

Motar ta dauka man fetur ne yayin da taki sarrafuwa a hanun direbanta, tayi hadari a kan titi.

Wani wanda abin ya faru a gaban idanunsa, ya shaidawa manema labarai cewa motar tayi hadari da kimanin karfe 3:30 na yamma.

“Babu wanda ya san adadin mutanen da suka mutu yanzu haka. Mutane suna cikin rafin suna harkokin gabansu, sai motar ta kubuce. Daga nan ta fai, ta tarwatse a kan gadar. Abin babu kyawun gani. Mafi munin abin da na taba gani tun da nake a rayuwata.” – Inji  Usman Ahmed dake zaune a garin Ankpa .

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments