Gwamna Abba Kabir ya magantu akan gina sabon shataletalen gidan Gwamnati da ya rushe

Daga ADAMU DABO

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada aniyarta na sake Gina sabon shataletale da ta rushe a hanyar shiga gidan gwamnati, zuwa hanyar kan titin gadar Sama dake Na’ibawa

Bayanin Hakan ya fito ne daga gwamnan jihar Kano Engr.Abba Kabir Yusuf a yayin ganawarsa da Mai zanan taswirar shataletalen Edifice kaltume Hana a Saban gurin da za a gudanar da wannan aiki

A jawabinta Mai zanan taswirar ta ce hakika wajen ginin shataletalen ya dace zai Kuma kawatar da zarar an kammala aikin

Ta Kuma godewa gwamnan jihar Kano bisa wannan dama da aka Bata ta amfani da zanan taswirar da ta Yi da jimawa

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments