Dangin AA Rufa’i na gaf da daukar matakin shari’a ga masu yamadidi da shi

Dangin A.A Rufa’i da ake ta yada bidiyonsa a kafafen sadarwa da sunan nishadi sun ce za su soma daukar matakin shari’a ga masu yin hakan.

Dangin sun bayyana hakan ne a Yayin ziyarar da suka kai gidan Rediyon Dala FM da ke birnin Kano tare da A A Rufa’i.

Kazalika sun yi bayani a kan rashin lafiyar da A A Rufa’i yake fama da ita, da kuma irin kokarin da suke yi wajen nema masa magani.

A karshe sun bukaci masu son taimaka masa don ya samu lafiya su tuntube su bawai su rika yamadidi da shi ba.

Kana sun ce kofa a bude take don taimaka masa

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments