Cutar Kwalara ta hallaka fiye da mutane 20 a jihar Cross River

Rahotanni na nuni da cewa, an samu barkewar cutar kwalara a jihar Cross River dake kudancin Kasar nan, inda ya zuwa yanzu cutar ta haddasa mutuwar mutane kimanin  25.

A cewar jami’an lafiya na yankin, ya zuwa yanzu, an kwantar da mutane fiye da 30 da suka kamu da cutar.

Sai dai tuni Gwamnatin  ta  tura kwararrun ma’aikatan lafiya  da kayan aiki zuwa kauyuka da cutar ta shafa, don hana cutar ci gaba da yaduwa.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
1 Comment
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments