Bayan karbar rantsuwa, Engr. Abba Kabir ya nada sakataren gwamnati da wasu muhimman Mukamai

Gwamnan Jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya gudanar da nada-naden mukamin na farko a gwamnatin sa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Wadanda aka nada mukaman sun haÉ—a da:

1. Hon. Shehu Wada Sagagi, Shugaban Ma’aikata

2. Abdullahi Baffa Bichi, sakataren gwamnatin jihar Kano

3. Dr. Farouq Kurawa
Babban Sakataren gwamnan wato PPS

4. Hon. Abdullahi Ibrahim Rogo, Shugaban tsare-tsare na gwamna

5. Sanusi Bature Dawakin Tofa, Babban Sakataren Yada Labarai

Sanarwar ta ce an zabi Wadannan nade-naden sun fara aiki ne daga yau Litinin 29 ga Mayu, 2023. Kuma an zabi wadanda aka nada ne bisa la’akari da tarihinsu, sadaukarwa da amincin su.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments