Bayan cire kudin makarantar kangararru gwamnan jihar Kano ya zayyana ayyukan da zai sa gaba

Gwamnan jihar Kano Engr Abba kabir Yusuf wanda aka fi Sani da Abba Gida-gida ya bayyana cewa zai dora tubalin gwamnatin sa akan ta tsohon gwamna sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Kabir ya bayyana hakan ne jim kadan bayan karbar rantsuwa inda ya fita ran-gadi zuwa wasu maaikatu da makarantu mallakar gwamnatin jihar Kano

Gida-gida ya Sami ziyartar gurare da dama ciki harda makarantar kangararru dake karamar hukumar Kiru inda a take ya mayar da ita kyauta ga duk Wanda yaje karatu makarantar

Kazalika gwamnan yayi alkawarin dawo da aikin yashe kogin jakara tare da shimfida masa kwalta da fitilu kamar yadda sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya kudurta.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments