• About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
No Result
View All Result
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
Home HAUSA NEWS

Asirin wasu kashe dake daukar nauyin taaddanci a Somalia ya fara tonuwa

Aksam Media by Aksam Media
January 2, 2023
in HAUSA NEWS
0
0
SHARES
Share on FacebookShare on Twitter

Manufar haddasa rikici a Somaliya da ci gaban da aka samu a halin yanzu
Manufar haddasa rikici a Somaliya da ci gaban da aka samu a halin yanzu

Kasar Somaliya dake gabashin Afrika ta kasance cikin ajandar kasashen duniya shekaru da dama da suka gabata sakamakon yunwa da ta’addanci da rigingimun siyasa suka haddasa. Kungiyar ‘yan ta’adda ta al-Shabaab tana yakar Gwamnatin Somaliya tun tsakiyar shekarun 2000. Kungiyar da ta yi nasarar kwace wasu yankunan kasar, tana kuma kai hare-hare kan fararen hula a wasu kasashe makwabta a yankin gabashin Afrika kamar Habasha, Djibouti da Kenya. Don haka, wannan barazanar ta’addancin na tasiri a yankin. Bisa wannan batun, an yi nazari kan manufofin tsaro dangane da siyasar cikin gida na Hasan Sheikh Mohamud, wanda aka zaba a matsayin Shugaban kasar Somaliya a ranar 15 ga watan Mayun shekarar 2022, da kuma abubuwan da ke faruwa a halin yanzu a yakin da ake yi da kungiyar ta’addanci ta al-Shabaab.

RelatedPosts

Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara

Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara

March 29, 2023
Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

March 29, 2023

Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 80 a kan dan wasan gaba na Tottenham.

March 29, 2023

Zamu gabatar da bayanan nazarin Kaan Devecioglu, Masanin Harkokin Arewacin Afrika akan batun…

Babban batun da ya fito fili a Somaliya a ‘yan makonnin nan shi ne dawowar sojojin Somaliya da aka horar a Eritrea. A cikin wannan yanayi, Shugaban Somaliya, Hasan Sheikh Mohamud, ya fitar da wata sanarwa a ranar Litinin, 19 ga watan Disamba, inda ya bayyana cewa sojojin da suka kwashe watanni suna atisaye a kasar Eritrea, za su fara komawa Somaliya nan da kwanaki masu zuwa kuma rukunin farko za su isa Mogadishu, babban birnin kasar a ranar 22 ga watan Disamba. Bugu da kari, an tattauna halin da wadannan sojoji ke ciki a kasar Eritrea a tsarin siyasar cikin gida na Somaliya a zamanin mulkin magabacin Mohamud, Mohamed Farmaajo. Tattaunawar ta haifar da martani a cikin gida tare da zargin an aike da wadannan sojojin zuwa yankin da ake yaki a Tigray na Habasha. A yayin ziyarar da Shugaban kasar Somaliya Sheikh Mohamud ya kai kasar Amurka, an bayyana a wani dandalin tattaunawa da ‘yan kasar Somaliya suka shirya cewa sojojin za su fara dawowa kafin karshen watan Disamba. Mohamud ya kuma bayyana cewa an amince da komai kan wannan batu kuma ba za a kara samun tsaiko ba. An kuma bayyana cewa, Mohamud, wanda ya yi alkawarin dawo da sojojin da ke kasar Eritrea a lokacin yakin neman zabe a lokacin bazara, ya ziyarci sansanonin horar da su a kasar ta Eritrea a watan Yulin da ya gabata. Iyalan sojojin da ba su ji ta bakin ‘yan uwansu ba, sun jaddada cewa suna son samun bayanai kan makomarsu a zanga-zangar da suka gudanar a bana. Mohamed Abdelsalam Babiker, Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na Musamman Kan Kare Hakkin Bil’adama a Eritrea, ya bayyana a shekarar da ta gabata cewa, sojojin Somaliya sun raka sojojin Eritrea da ke marawa sojojin Habasha baya a sansanonin horar da sojoji a Eritrea. A karshen watan Mayu ne Shugaban kasar na wancan lokaci, Mohamed Farmaajo ya sanar da cewa sun tura sojoji kusan dubu 5 zuwa kasar Eritrea don samun horo, amma an jinkirta dawowar sojojin domin kada a kawo cikas ga zaben ‘yan Majalisar Dokoki da na Shugaban kasa.

Wani muhimmin al’amari na tsaro a Somaliya shi ne hare-haren Kungiyar ta’addanci ta al-Shabaab da aka shafe sama da shekaru 20 ana kai wa. A cikin wannan muhallin, an yi rikodin  manyan lamurka biyu da suka afku a kwanan nan. Na farko dai shi ne harin da Kungiyar al-Shabaab ta kai a wani yanki da ke kusa da iyakar Somaliya a gabashin Kenya. A cewar ‘yan sanda da sojoji, ‘yan ta’addar al-Shabaab sun kai hari kan motar ‘yan sanda a gabashin Kenya, inda suka kashe ‘yan sanda biyu da farar hula daya. Kungiyar al-Shabaab ta fada a wani sanarwa da aka watsa kai tsaye ta rediyo cewa, wasu ‘yan bindiga sun kashe jami’an tsaron Kenya biyu tare da jikkata wasu da dama. A cikin sanarwar da Rundunar ‘Yan Sandan Kenya ta fitar, an bayar da rahoton cewa motar ‘yan sandan ta taka wani bam da aka yi da hannu a kan hanyarta daga Sansanin Hayley Lapsset (inda ‘yan gudun hijirar Somaliya da suka tsere daga ta’addancin al-Shabaab suke) zuwa garin Garissa, game da kilomita 120 daga iyakar Somaliya. A wata sanarwa da wani jami’in ‘yan sanda ya fitar, an bayyana cewa ‘yan bindiga sun kuma kai hari kan motar da makaman roka. Shugaban kasar Somaliya, Hassan Sheikh Mohamud ya bayyana cewa ‘yan ta’adda a Somaliya na fuskantar matsin lamba tun watan Agusta, lokacin da aka kaddamar da wani gagarumin farmaki kan Kungiyar al-Shabaab tare da goyon bayan Amurka da ATMIS da kuma mayakan sa kai na cikin gida.

Wani babban ci gaba kwanan nan dangane da al-Shabaab bisa bayanin da sojojin Somaliya suka yi, shi ne kashe ‘yan ta’adda 150, 5 daga cikinsu ‘yan kasashen waje, ta hanyar tsarkake yankin Shabelle ta tsakiya daga ‘yan ta’adda. A cikin wannan yanayi, Kakakin Ministan Tsaron Somaliya, Abdullahi Ali Anod ya shaida wa manema labarai a Mogadishu, babban birnin kasar a ranar Alhamis 22 ga watan Disamba cewa, an kwato birnin Runirgod mai matukar muhimmanci daga Kungiyar al-Shabab tare da goyon bayan mayakan sa kai. A cikin sanarwar an kuma bayyana cewa wannan ne birni mai muhimmanci na karshe da ‘yan ta’addar al-Shabaab da ke da alaka da Al-Qaeda suka kwace a yankin Shabelle ta tsakiya na kasar Somaliya. Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen kasar, Anod ya bayyana cewa da sanyin safiyar Alhamis ne sojojin kasar suka kaddamar da farmaki a kauyukan da ke kewayen garin inda suka yi artabu da ‘yan ta’addar. Yayin da sojojin Somaliya ba samu asarar rayuka ba sakamakon rikicin, 5 daga cikin ‘yan ta’addan da aka kashe a rikicin ‘yan kasashen waje ne wadanda ba a iya tantance kasashensu ba.

Bayan zaben Hassan Sheikh Mohamud a matsayin Shugaban kasa a Somaliya, ana gudanar da aiyuka akai-akai kan al-Shabaab. Kasashen waje kamar Türkiye, Amurka da Birtaniya, wadanda ke ba wa Somaliya kayan aikin tsaro da horar da sojojinsu na tsawon shekaru, suna taka muhimmiyar rawa wajen kara ingancin aiyukan. Ana sa ran kawo karshen barazanar ta’addancin da Kungiyar al-Shabaab ke yi a Somaliya nan da wani matsakaicin wa’adi, idan ma ba a cikin kankanin lokaci ba.

ShareTweetSendSharePin
Previous Post

Bikin sabuwar shekara mutane tara sun rasa rayuwar su a Uganda

Next Post

Yadda Gidauniyar kabiru Dalladi Bello ta tallafawa marasa lafiya da kudaden magani bayan fito da wasu fursinoni da tayi

Aksam Media

Aksam Media

RelatedPosts

Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara
HAUSA NEWS

Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara

by Aksam Media
March 29, 2023
0

Rundunar sojin Rasha ta yi amfani da tsarin Tornado-G wajen harba rokoki da dama a lokaci guda kan cibiyoyin sojan...

Read more
Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

March 29, 2023
Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 80 a kan dan wasan gaba na Tottenham.

Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 80 a kan dan wasan gaba na Tottenham.

March 29, 2023
Abubuwan da ya kamata ku sani gameda sabon shugaban PDP na rikon kwarya

Abubuwan da ya kamata ku sani gameda sabon shugaban PDP na rikon kwarya

March 29, 2023
Dalilan da suka hana Priyanka Chopra yin finafinai a India

Dalilan da suka hana Priyanka Chopra yin finafinai a India

March 29, 2023
Damfara ta yanar gizo, Amurka ta yanke hukunci zaman kaso ga wani Dan Najeriya

Damfara ta yanar gizo, Amurka ta yanke hukunci zaman kaso ga wani Dan Najeriya

March 28, 2023
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Login
Notify of
guest
guest
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

March 10, 2023
Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

February 21, 2023
Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

March 29, 2023
INEC tayi umarnin kara gudanar da zabe a jihar Kogi

Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

March 19, 2023
CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

2
Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

1
Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

1
Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

1
Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara

Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara

March 29, 2023
Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

March 29, 2023
Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 80 a kan dan wasan gaba na Tottenham.

Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 80 a kan dan wasan gaba na Tottenham.

March 29, 2023
Abubuwan da ya kamata ku sani gameda sabon shugaban PDP na rikon kwarya

Abubuwan da ya kamata ku sani gameda sabon shugaban PDP na rikon kwarya

March 29, 2023
  • Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara
HAUSA NEWS

Makaman da ake Dari-dari kar Rasha tayi amfani da su akan Ukraine yanzu ta fara

Rundunar sojin Rasha ta yi amfani da tsarin Tornado-G wajen harba rokoki da dama a lokaci guda kan cibiyoyin sojan ...

March 29, 2023
Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe
HAUSA NEWS

Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

March 29, 2023
Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 80 a kan dan wasan gaba na Tottenham.
HAUSA NEWS

Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 80 a kan dan wasan gaba na Tottenham.

Manchester United na shirin gabatar wa Tottenham tayin fam miliyan 80 a kan dan wasanta na gaba dan Ingila Harry ...

March 29, 2023
Abubuwan da ya kamata ku sani gameda sabon shugaban PDP na rikon kwarya
HAUSA NEWS

Abubuwan da ya kamata ku sani gameda sabon shugaban PDP na rikon kwarya

Mataimakin shugaban babbar jam’iyyar adawar Najeriya PDP Umar Iliya Damagun ya zama mukaddashin shugaban jam’iyyar bayan saukar wucin gadi da ...

March 29, 2023
Dalilan da suka hana Priyanka Chopra yin finafinai a India
HAUSA NEWS

Dalilan da suka hana Priyanka Chopra yin finafinai a India

Fitacciyar tauraruwar fina-finan Indiya Priyanka Chopra ta bayyana dalilan da suak sa ta fice daga masana'antar shirye fina-finan ƙasar ta ...

March 29, 2023

Recent Comments

  • Ibrahim S kabara on Hukumar kula da ayyukan yan sanda ta raba lambobin kiran waya Dan sa Ido a ayyukan yan sanda a lokacin zabe
  • Abbas Jibril on Katu ta Yankewa AbdulJabbar Kabara Hukuncin Kisa ta hanyar Rataya
  • Walid Y Haris on Akwai Malaman cocin dake kallan batsa a yanar gizo ta wayoyinsu-Fafaroma
  • Abba Garba Sufi on Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.
  • Sani saadu aliyu on CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

No Result
View All Result
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

wpDiscuz