• About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio
AKSAM MEDIA
  • General News
  • National News
  • World News
  • Health
  • Sports
  • Technology
  • Metro
No Result
View All Result
  • General News
  • National News
  • World News
  • Health
  • Sports
  • Technology
  • Metro
No Result
View All Result
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
Home HAUSA NEWS

Ana ci gaba da luguden wuta a Sudan duk da ikirarin tsagaita wuta

Aksam Media by Aksam Media
April 19, 2023
in HAUSA NEWS
0
0
SHARES
Share on FacebookShare on Twitter

Da misalin karfe 4 na yamma agogon GMT, lokacin da ya kamata yarjejeniyar da aka ce an cimma din ta fara aiki, ana iya jiyo karar harbe-harbe a kafatanin birnin Khartoum.

Mutane suna ta tsere wa dag khartoum babban birnin Sudan bayan kwana hudu da fara yakin / Hoto: AFP

RelatedPosts

Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election

Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election

September 20, 2023
Just in: Students hit the streets, protest over 100 per cent school fees hike

Just in: Students hit the streets, protest over 100 per cent school fees hike

September 13, 2023

Gwamnan jihar kano, Abba Kabir Yusuf, yana da wasu muhimman abubuwa guda biyu: shugaban kungiyar yan kasuwa

September 11, 2023

An ci gaba da jin karar fashewar abubuwa a Khartoum babban birnin Sudan, kwana hudu da fara yakin da ya hallaka kusan mutum 200, duk da ikirarin tsagaita wuta da aka ce an yi.

Bayan shiga tsakanin da kasashen duniya suka yi, Kwamandan Rundunar Rapid Support Forces [RSF], Mohamed Hamdan Dagalo wanda aka fi sani da Hemetti, ya ce zai amince da yarjejeniyar tsagaita wuta ta tsawon sa’a 24 a ranar Talata, wanda rundunar sojin kasar ta ce ba ta da wata masaniya a kai, kafin daga baya kuma ta zargi RSF da karya ta.

Tuni Rundunar RSF ta soki gwamnatin da karya yarjejeniyar.

Da misalin karfe 4 na yamma agogon GMT, lokacin da ya kamata yarjejeniyar da aka ce an cimma din ta fara aiki, ana iya jiyo karar harbe-harbe a kafatanin birnin Khartoum, kamar yadda shaidu da yawa suka fada, kuma an ci gaba da jin hakan har zuwa dare.

“Har zuwa yanzu ana ci gaba da yakin a Sudan, ciki har da birnin Khartoum da sauran wurare. Babu alamar kawo karshen fadan,” a cewar mai magana da yawun Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres.

Dagalo ya sanar da batun yarjejeniyar ce bayan da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya ce ya yi magana da janar-janar din biyu inda “ya nemi a yi gaggawar tsagaita wuta.”

Ministocin Harkokin Wajen Kasashe Bakwai Masu Karfin Tattalin Arziki na G7, wadanda suka hada da Amurka, su ma a ranar Talata sun yi kira ga bangarorin biyu masu fada da juna da su yi gaggawar dakatar da yakin, a yayin da ake jin kararrakin fashewar abubuwa a Khartoum, inda mayakan sa kai masu rawani ke ta sintiri a kan titunan birnin.

Ministan Harkokin Wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan ya tattauna da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken, kan hanyoyin da za a bi a dakatar da fadan tare da kwantar da hankula a Sudan.

Amurka ta ce an bude wa wata tawagar jami’an diflomasiyyarta wuta sannan kuma an kai wa jakadan Kungiyar Tarayyar Turai hari a gidansa.

Kungiyoyin bayar da agaji sun ce ana ta satar kayayyakin kula da lafiya da sauran kayan agaji.

Akwai fargabar cewa rikicin ka iya bazuwa zuwa sauran sassan kasar ta hanyar kai hare-haren sama.

Ganau sun ce an girke manyan motoci masu dauke da bindiogin kakkabo jiragen sama a unguwannin mutane a Khartoum tun da safiyar ranar Talata.

An farfasa gilasai da tagogi na gidajen mutane da ofisoshi da dama a fadin birnin

ShareTweetSendSharePin
Previous Post

PDP ta sake korar wasu jigajigan ta guda biyu

Next Post

Dubun wani mai sana’ar PoS ta cika bayan yayi hafzi da Miliyon 280

Aksam Media

Aksam Media

RelatedPosts

Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election
HAUSA NEWS

Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election

by Aksam Media
September 20, 2023
0

Kano governorship election tribunal declares Nasiru Yusuf Gawuna of APC as the  winner of 2023 governorship election.

Read more
Just in: Students hit the streets, protest over 100 per cent school fees hike

Just in: Students hit the streets, protest over 100 per cent school fees hike

September 13, 2023
Gwamnan jihar kano, Abba Kabir Yusuf, yana da wasu muhimman abubuwa guda biyu: shugaban kungiyar yan kasuwa

Gwamnan jihar kano, Abba Kabir Yusuf, yana da wasu muhimman abubuwa guda biyu: shugaban kungiyar yan kasuwa

September 11, 2023
El’s Empowerment foundation empowered over 170 windows in Kano.(POWA)

El’s Empowerment foundation empowered over 170 windows in Kano.(POWA)

September 10, 2023
Kungiyar Direbobi ta Malan Kato na ci gaba da Jinjinawa gwamnan jihar Kano

Kungiyar Direbobi ta Malan Kato na ci gaba da Jinjinawa gwamnan jihar Kano

September 9, 2023
Za’a dawo da karɓar harajin kullum-kullum na Adaidai Sahu: KAROTA

Za’a dawo da karɓar harajin kullum-kullum na Adaidai Sahu: KAROTA

September 9, 2023
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Login
Notify of
guest
guest
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

March 29, 2023
Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

March 10, 2023
Kungiyar tagwaye ta kasa tayi wani abin al-ajabi a nan Kano

Kungiyar tagwaye ta kasa tayi wani abin al-ajabi a nan Kano

April 29, 2023
Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

February 21, 2023
CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

2
Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

1
Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

1
Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

1
Independence Day: Nigerians in London demand justice for NNPP government in Kano

Independence Day: Nigerians in London demand justice for NNPP government in Kano

October 1, 2023
AGILE’s commitment to enhancing the lives of adolescent girls through education and EMPOWERMENT

AGILE’s commitment to enhancing the lives of adolescent girls through education and EMPOWERMENT

September 27, 2023
BREAKING: Kano Imposes 24 Hours Curfew

BREAKING: Kano Imposes 24 Hours Curfew

September 20, 2023
Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election

Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election

September 20, 2023
  • Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

    Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Kungiyar tagwaye ta kasa tayi wani abin al-ajabi a nan Kano

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Jami’ar Tarayya ta Dutsimma FUDMA ta yaba da Karatun digiri da AKCOE ta ke bayarwa.

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Independence Day: Nigerians in London demand justice for NNPP government in Kano
Metro

Independence Day: Nigerians in London demand justice for NNPP government in Kano

Independence Day: Nigerians in London demand justice for NNPP government in Kano As part of 63rd independence celebration, Nigerians in ...

October 1, 2023
AGILE’s commitment to enhancing the lives of adolescent girls through education and EMPOWERMENT
Metro

AGILE’s commitment to enhancing the lives of adolescent girls through education and EMPOWERMENT

The Kano Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment (AGILE) deputy project coordinator, Salisu Idris, led a delegation of the ...

September 27, 2023
BREAKING: Kano Imposes 24 Hours Curfew
General News

BREAKING: Kano Imposes 24 Hours Curfew

*20TH SEPTEMBER 2023* *PRESS RELEASE* *ENFORCEMENT OF TWENTY-FOUR HOURS (24HRS) CURFEW BY KANO STATE GOVERNMENT* *… As Residents are Warned ...

September 20, 2023
Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election
HAUSA NEWS

Breaking: Tribunal Declares Nasiru Gawuna Winner Of Kano Governorship Election

Kano governorship election tribunal declares Nasiru Yusuf Gawuna of APC as the  winner of 2023 governorship election.

September 20, 2023
Igbo people react to president Tinibuʼs appointments
National News

Igbo people react to president Tinibuʼs appointments

The Senior Special Assistant to the President Bola Tinubu on Community Development (South East), Chioma Nweze has described her appointment ...

September 20, 2023

Recent Comments

  • Ibrahim S kabara on Hukumar kula da ayyukan yan sanda ta raba lambobin kiran waya Dan sa Ido a ayyukan yan sanda a lokacin zabe
  • Abbas Jibril on Katu ta Yankewa AbdulJabbar Kabara Hukuncin Kisa ta hanyar Rataya
  • Walid Y Haris on Akwai Malaman cocin dake kallan batsa a yanar gizo ta wayoyinsu-Fafaroma
  • Abba Garba Sufi on Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.
  • Sani saadu aliyu on CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

No Result
View All Result
  • General News
  • National News
  • World News
  • Health
  • Sports
  • Technology
  • Metro

© 2023 Aksam Meadia LLC

wpDiscuz