Dan Majalisar jiha da ya lashe zabe a jam’iyar NNPP a jihar Bauchi ya ziyarci Madugun jam’iyar su

A Daren jiya Asabar ne Zababben Dan Majalissar Jiha Mai Wakiltar karamar Jama’are Karkashin Inuwar Jam’iyyar NNPP Hon. Mubarak Haruna, Yakai was jagoran jam’iyar su na kasa Sanata Rabiu Musa  Kwankwaso Ziyarar Neman tabarraki.

Hon. Mubarak Haruna Mairakumi, ya gabatar wa da  kwankwaso takardar shaidar lashe Zabensa da hukumar Zabe mai zaman kanta  ta bashi.

Jagoran jam’iyar NNPP na kasa yayi wa Matashin Dan Majalissar Addu’a tare da sanya Albarka a gare shi kuma ya ja hankalin sa da ya  kasance Walkili Nagari. Domin Al-ummar sa, Suyi Alfahari Dashi..

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments