Yayin da talakwa ke sa ran yan Majalisa zasu yi maiyuwuwa wajan kara waadin amfani da tsofaffin takardun 1000, 500, 200 yan Majalisar sun tafi hutun wata guda

Majalisar dattawan ta tafi hutu har zuwa wata guda domin bai wa ‘ya’yan damar yin yaƙin neman zaɓe a babban zaɓen da ke kararatowa.

Shugaban majalisar dattawan ƙasar Sanata Ahmad Lawan ne ya bayyana haka a zaman majalisar na ranar Laraba.

Sanata Ahmad Lawan ya ce majalisar ta ɗage zamanta daga ranar Laraba domin bai wa ‘yan majalisar damar yin yaƙin neman zaɓensu domin sake dawowa majalisar ko kuma taimaka wa jam’iyyunsu domin samun nasara.

A karshe yayi addu’ar Allah ya bai wa waɗanda ke son sake komawa majalisar dattawan nasara a zaɓen da ke tafe”.

Haka kuma  ya yi kira ga hukumar zaɓen ƙasar da jami’an tsaro da su tabbatar da cewa an gudanar da sahihi kuma amintaccen zaɓe a ƙasa ba tare da samun tashin hankali ba.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments