Za a dauki kwanaki uku ana fiskantar tsawa da Ruwan sama mai tsanani a wasu sassan Najeriya: NiMet

Hukumar NIMET  ta bayyana cewa Jihohin Sokoto, Zamfara, Kebbi, Yobe, Borno, Taraba da Adamawa zasu Iya fuskantar Ruwa da matsananciyar tsawa na tsawan kwanaki uku daga safiyar yau Jumma’a  19-08-2022

Rahoton da hukumar ta kula da yanayin sararin samaniya ta kasa ta fitar a yammacin Jiya alhamis shine ya tabbatar da hakan.

Kazalika tace yana zai Iya game jihohin Jigawa, Sokoto, Kaduna, Bauchi, Gombe, Zamfara, Kano, Katsina, Borno, Yobe da kuma Kebbi.

Ta kara da cewa yanayin ka Iya hadawa da yankin Arewa ta tsakiya inda jihohin Kwara, Niger da Abuja zasu Iya fuskantar Ruwa mai tsanani.

Haka yanayin zai kasance a jihohin Arewa ta tsakiya wato Abuja Benue, Kogi, Plateau da Nasarawa

Daga kudancin Kasar nan kuwa A safiyar yau Jumma’a jihohin Rivers da Akwa Ibom ruwa zasu samu jifajifa

Sai kuma Ekiti, Ondo, Ogun, Oyo, Osun, Enugu, Imo, da Edo zasu Fiskaci yanayin Ruwa sama-sama

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments