• About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
No Result
View All Result
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
Home HAUSA NEWS

Yan Najeriya sun gaza samun saukin kayan abinci du da faduwar da Dalar Amurka tayi da kaso 20.8

Aksam Media by Aksam Media
November 15, 2022
in HAUSA NEWS
0
0
SHARES
Share on FacebookShare on Twitter

Duk da cewa Naira ta fara farfadowa daga faduwa da ta yi a cikin makonnin 2 da suka gabata har ta kai ga naira 910 a bisa dala 1 wanda yanzu an sami farfadowa da kaso 20.8, naira ta koma 720 a bisa kowacce dala 1, masana tattalin arziki na ganin salon da aka dauka ne ke karya darajar Nairar.

Alkaluman kididdiga daga kasuwannin canjin bayan fagge na biranen Abuja, Legas, Kano, Fatakwal da dai sauransu, sun yi nuni da cewa farashin dala ya fadi a ‘yan kwanakin nan, lamarin da bai yi tasiri wajen rage tashin farashin kayayyakin masarufi a kasuwannin cikin kasar ba.

RelatedPosts

Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya

Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya

April 1, 2023
Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu

Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu

April 1, 2023

Masarautar Kano ta daga darajar wasu Hakimai tare da nada wasu sababbi

March 31, 2023

‘Yan Najeriyar dai na kokawa a game da yadda ba’a iya samun sauki a bisa farashin kayan abinci a kasuwa ko da an sami sauki a faduwar darajar naira kamar yadda ake gani tun ranar Litinin da ta gabata da naira ta sami karfi a kan dala daga 805 zuwa 720 a yanzu.

Wannan al’amarin ya shafi kama daga iyaye mata, masu kanana da matsakaitan sana’o’i kamar na abinci, sarrafa kujeru da dai sauransu sun bayyana cewa, ‘yan kasa na cikin mawuyacin hali.

Fitacciyar ‘yar kasuwa a fannin abinci da sarrafa kujeru, Laylah ali Othman, ta ce kamata ya yi gwamnatin kasar ta duba batun sa ido a kayyade farashin kayayyakin masarufi.

A dandalin sada zumunta na Tuwita, ‘yan Najeriya na dora alhakin faduwar darajar Naira a kan shugaban babban bankin kasar, Godwin Emefiele inda suke yi masa suka musamman ma bayan da faifan bidiyonsa da ya ke kalubalantar mai kamfanin kasuwar canjin kudi na bayan fagge da ke kayyade farashin canjin dalar Amurka a kan naira wato Aboki FX, da ake ganin kamfanın yake sanadın tashin farashin dala a Najeriya.

Mai sharhi a kan al’amurran yau da kullum, Mal. Baba Yusuf, ya ce salon tattalin arzikin da Najeriya ta dauka ne babban kalubale da ke karya lagon darajar kudin kasar wato naira, har yake shafar dukannin ‘yan kasar ciki har da talakwa.

Tuni dai gwamnatin Najeriya ta babban bankin CBN ta fara daukan matakai da take ganin zasu taimaka wajen farfado da tattalin arzikinta da kuma daga darajar Naira kamar sauya launin kudaddenta wato naira 200, 500 da dubu 1.

Sai dai shugaban kungiyar masu gudanar da ayyukan canji na Najeriya, Aminu Gwadabe, ya bayyanawa manema labarai cewa sake fasalin kudin naira ne ya sa ake fuskantar hauhawar farashin dala musamman a cikin makonni biyu da suka gabata.

ShareTweetSendSharePin
Previous Post

Kotu ta rushe zaben Dan takarar gwamna a wata jiha

Next Post

Peter Obi, was playing a game with his election bid: ex Anambra governor, Charles Soldotna.

Aksam Media

Aksam Media

RelatedPosts

Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya
HAUSA NEWS

Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya

by Aksam Media
April 1, 2023
0

Fitaccen mawakin nan da ke sharafi a wannan zamani, Hamisu Breaker ya musanta zargin da ake yi na cewa shi...

Read more
Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu

Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu

April 1, 2023
Masarautar Kano ta daga darajar wasu Hakimai tare da nada wasu sababbi

Masarautar Kano ta daga darajar wasu Hakimai tare da nada wasu sababbi

March 31, 2023
INEC ta mika shahadar lashe zabe ga zababben gwamnan jihar Kaduna

INEC ta mika shahadar lashe zabe ga zababben gwamnan jihar Kaduna

March 31, 2023
Russia ta kama wani Dan Amurka mai leken asiri

Russia ta kama wani Dan Amurka mai leken asiri

March 30, 2023
Hanya mai sauki da zaka hana sauro rayuwa a inda kake

Hanya mai sauki da zaka hana sauro rayuwa a inda kake

March 30, 2023
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Login
Notify of
guest
guest
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

March 10, 2023
Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

March 29, 2023
Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

February 21, 2023
INEC tayi umarnin kara gudanar da zabe a jihar Kogi

Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

March 19, 2023
CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

2
Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

1
Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

1
Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

1
Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya

Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya

April 1, 2023
Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu

Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu

April 1, 2023
Masarautar Kano ta daga darajar wasu Hakimai tare da nada wasu sababbi

Masarautar Kano ta daga darajar wasu Hakimai tare da nada wasu sababbi

March 31, 2023
INEC ta mika shahadar lashe zabe ga zababben gwamnan jihar Kaduna

INEC ta mika shahadar lashe zabe ga zababben gwamnan jihar Kaduna

March 31, 2023
  • Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Rarara ya saki zazzafar Wakar da yayi wa Abba Gida-gida ta cin zabe

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya
HAUSA NEWS

Dalilin da yasa Breaker yace Babu wata alaƙar soyayya tsakanin sa da Rukayya

Fitaccen mawakin nan da ke sharafi a wannan zamani, Hamisu Breaker ya musanta zargin da ake yi na cewa shi ...

April 1, 2023
Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu
HAUSA NEWS

Bayan karbar kaddamar faduwa da Gawuna yayi APC ta garzaya kotu

Babbar Jam’iyar adawa a Kano APC ta bayyana shirin ta na zuwa kotu domin kalubalantar sakamakon zaben da hukumar zabe ...

April 1, 2023
Masarautar Kano ta daga darajar wasu Hakimai tare da nada wasu sababbi
HAUSA NEWS

Masarautar Kano ta daga darajar wasu Hakimai tare da nada wasu sababbi

Daga khadija Abdullahi Aliyu Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya daga Darajar wasu Hakimansa da kuma nada ...

March 31, 2023
INEC ta mika shahadar lashe zabe ga zababben gwamnan jihar Kaduna
HAUSA NEWS

INEC ta mika shahadar lashe zabe ga zababben gwamnan jihar Kaduna

Hukumar Zabe Mai Zaman Katta Ta Kasa INEC, yau tabawa zabban Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Malam Uba Sani shedar sakamako yin ...

March 31, 2023
Russia ta kama wani Dan Amurka mai leken asiri
HAUSA NEWS

Russia ta kama wani Dan Amurka mai leken asiri

An kama wani ɗan jaridan Amurka da ke aiki da jaridar Wall Street Journal a Rasha inda aka zarge shi ...

March 30, 2023

Recent Comments

  • Ibrahim S kabara on Hukumar kula da ayyukan yan sanda ta raba lambobin kiran waya Dan sa Ido a ayyukan yan sanda a lokacin zabe
  • Abbas Jibril on Katu ta Yankewa AbdulJabbar Kabara Hukuncin Kisa ta hanyar Rataya
  • Walid Y Haris on Akwai Malaman cocin dake kallan batsa a yanar gizo ta wayoyinsu-Fafaroma
  • Abba Garba Sufi on Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.
  • Sani saadu aliyu on CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

No Result
View All Result
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

wpDiscuz