Yadda PDP take nuna farin cikinta a fili da barakar APC akan Muslim Muslim tiket

Kakakin kwamitin yakin neman zaben Atiku Abubakar, Daniel Bwala, ya nuna farin cikin sa da yadda  Osinbajo da Boss Mustapha suka ce a cire daga kwamitin kamfen din APC.

Bwala, ya ce rashin goyon bayan tikitin musulmi musulmi a jam’iyyar  APC ta yi ne yasa suka janye daga kwamitin yakin neman zaben

Festus Keyamo, mai magana da yawun kamfen din Tinubu/Shettima ya yi martani yana mai cewa ba a saka Osinbajo da Mustapha bane don su mayar da hankali kan aiki

Daniel Bwala, kakakin kwamitin yakin neman zaben Atiku Abubakar ya ce ya jinjinawa mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da Boss Mustapha, sakataren gwamnatin tarayya, SGF, saboda ‘kin amincewa’ da tikitin musulmi da musulmi na jam’iyyar APC

Mun jinjinawa jarumtar Farfesa Osinbajo da Boss Mustapha saboda kin amincewa da tikitin MM ta hanyar cewa kada a saka su a kwamitin kamfen din APC. Ka da ku yarda da siyasar addini. Yan Najeriya za su raba gardama a yayin zabe.”

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments