Yadda Osinbajo ya amince da bude jami’ar yanar gizo da Karin wasu 35

Mataimakin shugaban Najeriya, Yemi Osinbajo ya amince wa ‘yan kasuwa su kafa sababbin jami’o’i 36 a kasar nan.

Farfesa Yemi Osinbajo ya bada damar kafa jami’o’in ne a lokacin da ya jagoranci zaman majalisar FEC kamar yadda jaridar The Nation ta rahoto.

Majalisar zartarwa ta duba takardu 40 daga ma’aikatu, cibiyoyi da hukumomi dabam-dabam, daga nan aka bada lasisin kawo sababbin jami’o’i.

Ministan ya ce a cikin jami’o’in da aka kafa har da wanda za ta rika aiki ta yanar gizo, a karon farko kenan da aka kafa irinta a fadin kasar nan.

An ruwaito Adamu na cewa jami’ar da za a samar a jihar Bauchi za ta taimaka musamman ga matan Arewa da ke Dari-dari wajan gogayya da maza.

A bayaninsa, Ministan ilmin bai fadi sunan jami’o’in da za a kafa ba, illa iyaka ya nuna akwai bukatar karin jami’o’i saboda masu sha’awar karatu.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments