Yadda Mataimakin shugaban kasa ya nemi afuwar Musulman Nageriya.

Maitamakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce yana neman afuwar al’ummar Musulmi bisa wasu kalamai da ya yi game da zaɓen shugabannin majalisar dokokin Najeriya.

A cewarsa ba a fahimci maganar a muhallinta ba, kuma ba shi da wata manufa na ɓata sunan addininsa.

Sanata Kashim a tattaunawarsa da BBC ya ce ya yi waɗannnan kalamai ne saboda maslahar Najeriya, ganin cewa suna da wasu bayanan sirri da bai dace ya fito bainar jama’a yana bayani a kansu ba.

Sannan yadda lamura ke tafiya a Najeriya a wannan lokaci, dole shugabanni su fito su ja hankali domin wanzuwar ƙasar baki-ɗaya.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments