Tinibu ya sanya daliba mai karatun Digree cikin kwamitin sauya fasalin hanyoyin tattara kudin shiga

Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya kafa kwamiti na musamman da zai kawo gyare-gyaren manufofin tattalin arziki a Najeriya.

Tashar yada labarai ta Channels TV ta ce an yi bikin kaddamar da kwamitin a fadar Aso Rock Villa da ke birnin tarayya Abuja.

Mai taimakawa Shugaban Najeriya wajen harkoki na musamman, sadarwa da dabaru, Dele Alake ne ya fitar da sanarwa hakan a ranar Talata.

Kwamitin zai zama karkashin jagorancin kwararren masani a harkar haraji da kudi kuma shugaba a Prince Water house Coopers, Taiwo Oyedele.

Taiwo Oyedele da sauran ‘yan kwamitin da aka zakulo dagaciki da wajen gwamnati za su taimaka wajen kawo dokoki da duk tsare-tsaren tattali.

Jaridar Punch ta ce kwamitin zai fito da hanyoyi tare da tsara yadda za a rika tattara haraji a Najeriya ba tare da an rika samun tufka da warwara ba.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments