Kwamishinan zaben Adamawa ya magantu akan zargin an bashi Biliyan biyu.

Shugaban hukumar zaben ta INEC a jihar Adamawa da aka dakatar, Barrister Hudu Yunusa Ari ya musanta zargin da ake yi cewa ya karbi cin hanci na Naira biliyan biyu don ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta yi nasara a zaben na gwamnan jihar Adamawa.

Binani dai ita ce ‘yar takarar gwamna ta jam’iyar APC a jihar Adamawa a zaben 2023.

Ta kalubalanci gwamna mai ci ne na jam’iyar PDP Ahmadu Umaru Fintiri wanda a karshe hukumar zaben ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben a wa’adi na biyu.

Hudu ya ce ba ya nadama ko kadan game da matakin da ya dauka na sanar da sakamakon zaben gwamnan da aka yi a jihar ana tsakiyar tattara sakamako.

Barrister Hudu Yunusa wanda rundunar `yan sanda ke nema ya ce doka ce ta ba shi hurumin sanar da sakamakon.

Ya kara da cewa a shirye yake ya mika kansa ga rundunar ‘yan sandan Najeriya da ke nemansa nan ba da jimawa ba.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments