Kimanin kaso daya bisa hudu na yan Najeriya suna fama da cutar tabin hankali: Taiwo Obindo

RelatedPosts

Obindo wanda ke jagorancin Tsangayar kula da masu fama da tabin hankali, a Cibiyar horar da likitoci ta Afirka ta Yamma dake Najeriya, ya bayyana cewar halin kula da masu fama da cutar tabin hankali a Najeriya ya tabarbare, ganin yadda alkaluma suka nuna cewar kasar na dauke da mutane sama da miliyan 60 dake fama da matsalar.

Masanin ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Najeriya cewar, abin takaici shine kashi 90 na wadannan mutane dake fama da matsalar basu da hanyar zuwa asibiti domin samun kula daga likitoci, sai kashi 10 kacal wadanda basu da yawa.

Daga cikin matsalolin da masanin ya gabatar a matsayin wadanda ke hana masu fama da cutar samun magani, sun hada da rashin bayani dangane da abinda ke haifar da cutar da kuma yadda ake kula da ita, da kuma yadda hukumomin Najeriya ke yiwa matsalar rikon ko-in-kula da kuma al’adar wasu ‘yan Najeriya dangane da matsalar, sai kuma karancin kwararrun likitocin dake kula da masu fama da cutar.

Obindo ya kuma bayyana karancin asibotocin da ake kula da masu fama da cutar, ganin cewar akasarin jihohin da suke da su, sun sanya su ne a birane, yayin da sama da kasha 60 na jama’ar Najeriya ke zama a yankunan karkara.

Masanin ya bukaci sake fasalin kula da lafiyar ‘yan Najeriya domin sanya shirin kula da masu fama da tabin hankali a cikin ayyukan kananan asibitocin dake yankunan karkara.

RelatedPosts

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments
popular Nigerian pastor says God is not Christian

popular Nigerian pastor says God is not Christian

Popular pastor, Abel Damina, has explained why God is not a Christian while charging his congregations to stop believing that ...

Just IN:Tinubu re-elected as ECOWAS chairman

Just IN:Tinubu re-elected as ECOWAS chairman

President Bola Ahmed Tinubu has been re-elected for another one-year tenure as Chairman of the ECOWAS Authority of Heads of ...

Iran threatens war if Israel attacks Lebanon

Iran threatens war if Israel attacks Lebanon

Iran on Saturday warned that “all Resistance Fronts”, a grouping of Iran and its regional allies, would confront Israel if ...

Why Dangote re, seek FG intervention as marketers opt for fuel import

Why Dangote re, seek FG intervention as marketers opt for fuel import

Operators in the downstream oil sector, on Monday, called on the Federal Government to intervene by ensuring the provision of ...

Takaitattun labaran kwallon kafa

Takaitattun labaran kwallon kafa

Ana sa ran Manchester United za ta amince da biyan kusan fam miliyan 40, domin siyan dan wasan gaba na Netherlands, ...