Iran: Zanga-zangar kyamar hijabi fiye da mutane 50 sun rasa rayuwar su

Kamar yadda Kamfanin dillancin labarai na Borna ya tabbatar, yace karuwar adadin na zuwa ne a dai dai lokacin da ake samun karuwar masu shiga zanga-zangar kin jinin hijabi a karin birane da dama na kasar Iran

Kwana na takwas kenan ana ganin kakkarfar zanga-zangar a manyan biranen Iran ciki har da Tehran don nuna kyamarsu ga takurar da ake musu wajen tilasta su sanya hijabi ba da ra’ayinsu ba.

Tun farko dai zanga-zangar ta samo asali daga kamen Mahsa Amini ‘yar shekaru 22 da jami’an ‘yan sandan tabbatar da bin dokokin addini suka kama amma kuma kwanaki 3 bayan kamen suka sanar da mutuwarta, lamarin da ya sanya zargin ko su suka kashe ta .

Adadin mutanen da suka mutu a zanga-zangar Iran ya karu zuwa mutum 50, cikin mako guda da faro boren bayan kisan matashiya Mahsa Amini da ake zargin jami’an ‘yan sandan tabbatar da bin doka da aikatawa.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments