Ganduje ya saka labule da Dan takarar shugaban kasa na jam’iyar PDP

Abdullahi Umar Ganduje ya sa labule da Anyim Pius Anyim a gidansa da ke birnin tarayya Abuja

Zuwa yanzu ba a san abin da shugaban na APC ya tattauna da tsohon sakataren gwamnatin kasar ba

Dr. Ganduje ya sha alwashin karfafa jam’iyya mai mulki yayin da aka gagara gane manufar Anyim

Wasu su na ganin akwai yiwuwar Sanata Pius Anyim ya sauya-sheka daga PDP musamman ganin take-takensa a ‘yan kwanakin bayan nan

Za a iya tuna cewa tsohon shugaban majalisar dattawan ya ziyarci Mai girma shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar sa a kwanakin baya.

Yayin ziyarar, Olisa Metuh ya na tare da Anyim wanda ya rike matsayin sakataren gwamnatin tarayya a gwamnatin Dr. Goodluck Jonathan.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments