Home HAUSA NEWS Fashin baki dangane da taron ECOWAS da ta gudanar akan kasar Mali,...

Fashin baki dangane da taron ECOWAS da ta gudanar akan kasar Mali, Burkina Faso da Guinea

Bayan wani taro da shugabannin suka gudanar Jiya  a Birnin Accra na kasar Ghana domin karbar rahotanni daga kwamitocin da suka kafa da kuma shawarwari, shugabannin sun yanke hukuncin dage taron nasu zuwa watan Yuli mai zuwa domin bada damar ci gaba da tintibaar masu ruwa da tsaki.

Wata majiya daga wurin taron tace bayan tafka mahawara, na tsawan lokaci shugabannin sun kasa cimma matsaya akan matakin da ya dace a dauka akan kasar Mali, wadda taki gabatar da shirin mika mulki ga fararen hula da kuma katse hulda da kungiyar G5 Sahel dake yaki da ‘Yan ta’adda.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gabatar da matsayin kasar Najeriya  a wajen taron cewar, duk wani matakin ladabtarwar da za’a dauka akan sojojin a tabbatar da cewar ba zai yiwa jama’ar kasar illa ba.

Tuni kungiyar ECOWAS da AU suka sanar da dakatar da wadannan kasashe daga cikin su da kuma bukatar gabatar musu da shirin da sojojin ke da shi na mayar da mulki ga fararen hula.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments