Emefiele ya roki kungiyar kwadago da ta dakatar da yajin aikin da zata fara a ranar Laraba

Gwamnan babban bankin Najeriya CBN, Godwin Emefiele ya gana da ministan kwadago, criss Ngige, a yammacin yau Litinin 27-03-2023.

Ganin ya biyo bayan shirin kungiyar yan kwadago na shiga yajin aiki a ranar Laraba mai zuwa.

Emefiele ya roki Ministan da yasa baki wajen dakatar da yajin aikin da kungiyar ta dauki gabarar farawa a ranar Laraba.

Taron ya sami halartar manya daga kungiyar yan kwadago da kuma shuwagabanni daga babban bankin Najeriya CBN

Emefiele yace tuni ya wadata bankunan yan kasuwa da takardun kuÉ—i.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments