• About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
No Result
View All Result
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
Home HAUSA NEWS

Bankin Duniya yayi tsokaci game da sauya fasalin Naira da CBN yayi

Aksam Media by Aksam Media
December 27, 2022
in HAUSA NEWS
0
0
SHARES
Share on FacebookShare on Twitter

Sake fasalin naira da Babban Bankin Najeriya ya yi ya ja hankalin Bankin Duniya wato World Bank.

Babban Bankin Duniyan ya yi gargadi cewa sabon kudin na iya yin illa ga harkokin tattalin arzikin talakawan kasar da ma kananan masana’antu saboda gajeren lokacin da bankin Najeriya ya diba domin sauya tsofaffin kudaden zuwa sabbi.

RelatedPosts

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

March 25, 2023
Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

March 25, 2023

APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

March 24, 2023

Bankin Duniya wato World Bank mai Shelkwata a Washington DC ya bayyana gargadin a wani sabon rahoto ne da ya fitar a shafinsa na yanar gizo mai dauke da suna Nigeria Development Update a turance.

Bankin Duniya ya nuna cewa sabuwar manufar za ta iya yin illa ga kanana yan kasuwa musamman masu hada-hadar kudi na yau da kullum da kuma kananan masana’antu. Wani abu da kwararre a fannin tattalin arziki na kasa da kasa Shuaibu Idris Mikati ya ce gargadin da Bankin Duniya ya yi ba sabon abu bane.

Mikati yace Bankin Duniya na bada irin wannan shawarwari ga kasashe ko masu tasowa ko kasahen Turai wadanda suka riga suka cigaba.

Mikati ya ce wannan shawara ce aka bayar akan illoli da ka iya tasowa kan wannan sauyin launin wasu kudade da Bankin Najeriya ya yi.

Sake fasalin naira da Babban Bankin Najeriya ya yi ya ja hankalin Bankin Duniya wato World Bank.

ABUJA, NIGERIA —
Babban Bankin Duniyan ya yi gargadi cewa sabon kudin na iya yin illa ga harkokin tattalin arzikin talakawan kasar da ma kananan masana’antu saboda gajeren lokacin da bankin Najeriya ya diba domin sauya tsofaffin kudaden zuwa sabbi.

Bankin Duniya wato World Bank mai Shelkwata a Washington DC ya bayyana gargadin a wani sabon rahoto ne da ya fitar a shafinsa na yanar gizo mai dauke da suna Nigeria Development Update a turance.

Bankin Duniya ya nuna cewa sabuwar manufar za ta iya yin illa ga kanana yan kasuwa musamman masu hada-hadar kudi na yau da kullum da kuma kananan masana’antu. Wani abu da kwararre a fannin tattalin arziki na kasa da kasa Shuaibu Idris Mikati ya ce gargadin da Bankin Duniya ya yi ba sabon abu bane.

Mikati yace Bankin Duniya na bada irin wannan shawarwari ga kasashe ko masu tasowa ko kasahen Turai wadanda suka riga suka cigaba.

Mikati ya ce wannan shawara ce aka bayar akan illoli da ka iya tasowa kan wannan sauyin launin wasu kudade da Bankin Najeriya ya yi.

Mikati ya ce wannan shawara ce da ya kamata a duba domin ana cewa yan Najeriya sun kai miliyan 220 amma in an duba wadanda suke hulda da banki wadanda suke da lambar ajiya wato BVN, ba su wuce miliyan 60 ba.

Saboda haka wannan ya nuna cewa masu ajiya a bankuna ba su da yawa sosai. Mikati ya ce abu ne da Bankin Najeriya ya kamata ya duba saboda ya dauki mataki kaman yadda ya saurari koken mutane, wajen kara yawan kudin da za a cire a asusun bankuna.

Shi kuwa mai nazari a fanin tattalin arziki Yusha’u Aliyu ya yi tsokaci cewa tsarin yana da kyau amma ya kamata a fara shi daga manyan birane

Yasha’u ya ce Babban Banki yana da dama da zai gudanar da wannan tsari amma ya kamata ya yi la’akari da irin mutanen da ya kamata su yi amfani da tsarin musayar kudi ta dandalin yanar gizo wadanda yawancin su suna kauyuka ne kuma ba sa jin turanci balle su iya amfani da dandalin yanar gizo wajen mu’amala da kudi.

Yusha’u ya ce Babban Bankin Najeriya ya duba yadda zai yi gyara a wannan fannin domin ya kara yawan lokaci da za a iya musayar tsofaffin kudaden zuwa sababbin Kudade idan ba haka ba zai kawo rudami a harkar farfado da tattalin arzikin kasar ba ki daya.

Akan haka ne gagarabadan Majalisar Wakilai Mohammed Tahir Monguno ya sha alwashin tada maganar karin lokaci da ma ta wayar da kan al’umma musamman na Jihohin Borno da Yobe idan majalisa ta dawo daga hutun karshen shekara. Monguno ya ce yawancin kauyuka ba su da bankuna, kuma mutane dayawan gaske ba su da ilimin amfani da wayoyin su wajen mu’amalar kudi, gashi kuma ba kullum ake samun hanyoyin sadarwa ba.

Munguno ya ce zai dage har sai ya ga an samu sauyi a lokaci na yin chanjin kudaden.

Abin jira a gani shi ne irin matakin da Babban Bankin Najeriya zai dauka ganin cewa Bankin Duniya da ma yawancin yan kasa sun nemi a kara tsawon lokaci saboda a samu a sauya tsofaffin kudaden ba tare da an musguna wa kowa ba.

ShareTweetSendSharePin
Previous Post

China ta samar da jirgin saman fasinjoji mafi girma a Duniya

Next Post

Dankari, Sheikh Ahmad Gumi ya ‘Debo ta gaba daya

Aksam Media

Aksam Media

RelatedPosts

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO
HAUSA NEWS

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

by Aksam Media
March 25, 2023
0

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce kafin Amurka ta koma cikin hukumar raya...

Read more
Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

March 25, 2023
APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

March 24, 2023
CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

March 24, 2023
Matashi mai tattaki daga Garin Kubau zuwa Kaduna dan taya murna ga,  sen Uba Sani, tafiya ta nisa

Matashi mai tattaki daga Garin Kubau zuwa Kaduna dan taya murna ga, sen Uba Sani, tafiya ta nisa

March 24, 2023
Abubuwan da cin su ke hana shan wahalar Azumi komai rana

Abubuwan da cin su ke hana shan wahalar Azumi komai rana

March 24, 2023
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Login
Notify of
guest
guest
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

March 10, 2023
Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

February 21, 2023
Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

February 11, 2023
INEC tayi umarnin kara gudanar da zabe a jihar Kogi

Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

March 19, 2023
CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

2
Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

1
Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

1
Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

1
China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

March 25, 2023
Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

March 25, 2023
APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

March 24, 2023
CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

March 24, 2023
  • Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu an kama wani Dan Majalisa dauke da makuden kudaden waje

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO
HAUSA NEWS

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce kafin Amurka ta koma cikin hukumar raya ...

March 25, 2023
Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu
HAUSA NEWS

Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

Aliyu Muhammad ya tsallake rijiya da baya a 2019, saboda makauniyar soyayya daya samu kansa a ciki ta Shugaba Muhammadu ...

March 25, 2023
APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa
HAUSA NEWS

APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

Kwamatin yakin neman zaben na Dan takarar jam’iyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinibu ya musanta raderadin da wasu kafafen sadarwa ...

March 24, 2023
CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma
HAUSA NEWS

CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

Daga kabiru A Dukawa Babban bankin Najeriya CBN ya ci alwashin hukunta duk wani bankin yan kasuwa da ya samu ...

March 24, 2023
Matashi mai tattaki daga Garin Kubau zuwa Kaduna dan taya murna ga,  sen Uba Sani, tafiya ta nisa
HAUSA NEWS

Matashi mai tattaki daga Garin Kubau zuwa Kaduna dan taya murna ga, sen Uba Sani, tafiya ta nisa

Matashi mai suna Yusuf Umar ya ga dacewar zuwa Kaduna garin gwamna ne domin taya sabon zababben gwamnan jihar Kaduna ...

March 24, 2023

Recent Comments

  • Ibrahim S kabara on Hukumar kula da ayyukan yan sanda ta raba lambobin kiran waya Dan sa Ido a ayyukan yan sanda a lokacin zabe
  • Abbas Jibril on Katu ta Yankewa AbdulJabbar Kabara Hukuncin Kisa ta hanyar Rataya
  • Walid Y Haris on Akwai Malaman cocin dake kallan batsa a yanar gizo ta wayoyinsu-Fafaroma
  • Abba Garba Sufi on Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.
  • Sani saadu aliyu on CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

No Result
View All Result
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

wpDiscuz