An kafa kwamatin binciken yunkurin juyin mulki a Gambia

The Gambia Flag Against City Blurred Background At Sunrise Backlight

Gwamnatin Gambia ta kafa wani kwamitin hadin gwiwa mai kunshe da mambobi 11, domin bincike kan zargin yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba a makon da ya gabata.

Kakakin gwamnatin kasar Ebrima Sankareh, ya bayyana cikin wata sanarwa a jiya cewa, masu binciken na da kwanaki 30, farawa daga jiyan, domin bincike da shirya rahotonsu, tare da gabatar da shi.

Kawo yanzu, kasar dake yammacin Afrika ta tsare sojoji 8 da farar hula guda, wadanda ake rike da su domin bincike

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments