• About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
No Result
View All Result
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
Home HAUSA NEWS

Mun shafe shekaru 29 babu likita a asibitin garin mu: Alummar garin Zakirai

Aksam Media by Aksam Media
January 22, 2023
in HAUSA NEWS
0
0
SHARES
Share on FacebookShare on Twitter

Yadda al’ummar garin Zakirai a Kano su ka shafe shekaru 29 babu likita a asibitin garin

Daga Sadik Lamin Hassan

RelatedPosts

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

March 21, 2023
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

March 21, 2023

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

March 21, 2023

Al’ummar garin Zakirai da ke jihar Kano a arewacin Najeriya sun bayyana takaicinsu kan yadda su ka shafe shekaru 29 ba tare da gwamnati ta samar musu da babban likita a asibitin da aka gina tun lokacin mulkin gwamna Abdullahi Wase.

A shekarar 1994 ne gwamnatin jihar Kano ta gina asabitin na garin Zakirai kuma yana karkashin hukumar kula da lafiya a matakin farko ta jihar sai dai har wannan lokaci babu babban likita a asibitin.

Garin Zakirai wanda shi ne hedikwatar ƙaramar hukumar Gabasawa na da nisan kilomita 42 daga birnin Kano kuma garin yana da yawan mutane fiye da dubu dari ɗaya, sai dai al’ummar wannan gari na fuskantar kalubale daban-daban musamman a ɓangaren kiwon lafiya.

Wakilin Aksam Media ya tattauna da wasu daga cikin mutanen wannan gari na Zakirai inda su ka bayyana irin kalubalen da su ke fuskanta musamman a lokacin da mata su ka zo haihuwa ko kuma wata larura da ta ke bukatar babban likita.

Muhammadu Auwal daya ne daga cikin shugabannin matasa a yankin ya bayyana cewa baya ga rashin babban likita a asibitin kuma suna fama da rashin ma’aikata da za iya bayar da tallafi ga kananan cututtuka.

Haka kuma Muhammad Auwal ya ce asibitin na Zakirai ya zama wata matattara ta ma’aikatan wucin gadi da su ke cin karen su babu – babbaka ta hanyar sayar da magani ga marasa lafiya akan farashin da su ka ga dama.

“Tun da aka gina wannan asibitin a zamanin mulkin gwamna Abdullahi Wase ba a taba samun babban likita ba. A shekarun baya ana tura dan bautar ƙasa a matsayin likita, amma a halin yanzu sai ma’aikata wucin gadi da su ma su ke bukatar horo da karin ilimi akan abin da su ka karanta”

“Idan marar lafiya ya je domin a duba lafiyarsa tare da rubuta masa magani, a nan sai abin da ya gani domin ma’aikatan wucin gadi ne za su rubuta maganin kuma su sayar maka akan yadda su ka ga dama”

Hakazalika Muhammad Auwal ya kara da cewa duk da irin rashin likita da kwararrun ma’aikata da kuma kayan aiki amma hakan bai hana gwamnati yiwa asibitin rijista da inshorar lafiya ba duk da cewa babu magani a asibitin.

“Asibitin yana cikin asibitocin da gwamnatin jihar Kano ta yiwa rijista a matsayin wanda ma’aikata za su da iyalansu domin a duba lafiyarsu, anna abin takaicin shi ne babu magani a duk lokacin da larura ta kai mutum ko iyalansa”

A lokacin haɗa wannan rahoton Aksam Media ta yi kokarin tuntubar babban sakataren hukumar kula da lafiya a matakin farko ta jihar Kano, Dr. Tijjani Hussaini sai dai bamu same shi. Sai dai wata majiya daga hukumar ta bayyana mana cewa gwamnatin jihar Kano ta dauki manyan likitoci guda 25 da za ta tura su asibitocin da su ke ƙarƙashin ta.

ShareTweetSendSharePin
Previous Post

Kasar China ce ke rike Da ragamar tattalin arzikin Duniya : Ngozi Okonjo-Iweala

Next Post

Najeriya na shirin fara fitar da amfanin gona zuwa kasar China

Aksam Media

Aksam Media

RelatedPosts

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna
HAUSA NEWS

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

by Aksam Media
March 21, 2023
0

Rahotanni na nuni da cewa jam'iyun adawa da suka yi takarar gwamnan a jihar Kaduna sun yi watsi da sakamakon...

Read more
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

March 21, 2023
An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

March 21, 2023
Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

March 21, 2023
Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu

Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu

March 20, 2023
Yanzu-yanzu INEC ta sanar da Sanata  Uba Sani  a matsayin wanda ya ci zabe a jihar Kaduna

Yanzu-yanzu INEC ta sanar da Sanata Uba Sani a matsayin wanda ya ci zabe a jihar Kaduna

March 20, 2023
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Login
Notify of
guest
guest
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

March 10, 2023
Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

February 21, 2023
Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

February 11, 2023
INEC tayi umarnin kara gudanar da zabe a jihar Kogi

Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

March 19, 2023
CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

2
Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

1
Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

1
Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

1
Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

March 21, 2023
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

March 21, 2023
An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

March 21, 2023
Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

March 21, 2023
  • Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu an kama wani Dan Majalisa dauke da makuden kudaden waje

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna
HAUSA NEWS

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

Rahotanni na nuni da cewa jam'iyun adawa da suka yi takarar gwamnan a jihar Kaduna sun yi watsi da sakamakon ...

March 21, 2023
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina
HAUSA NEWS

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Dan takarar gwamnan jihar katsina  na babbar jam'iyyar hamayya ta PDP, a zaben da ya gabata, Sanata Yakubu Lado Dan ...

March 21, 2023
An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna
HAUSA NEWS

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

Daga Hassan Umar Gwammaja A dare jiya an samu mamakon ruwan sama mai karfi (Na farko a jihar Kaduna) wanda ...

March 21, 2023
Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna
HAUSA NEWS

Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cire dokar hana fita da ta kakabawa al'ummar jihar a jiya bayan ayyana Abba kabir ...

March 21, 2023
Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu
HAUSA NEWS

Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu

Shahararren jarumi kumaawaki a masana'antar Kannywood Baba Chinedu yace "An Sacè Mun Kaya Na Sama Da Milyan Gòma A Lokacin ...

March 20, 2023

Recent Comments

  • Ibrahim S kabara on Hukumar kula da ayyukan yan sanda ta raba lambobin kiran waya Dan sa Ido a ayyukan yan sanda a lokacin zabe
  • Abbas Jibril on Katu ta Yankewa AbdulJabbar Kabara Hukuncin Kisa ta hanyar Rataya
  • Walid Y Haris on Akwai Malaman cocin dake kallan batsa a yanar gizo ta wayoyinsu-Fafaroma
  • Abba Garba Sufi on Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.
  • Sani saadu aliyu on CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

No Result
View All Result
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

wpDiscuz